A cikin hudubar da babban liman ya gabatar a wannan ranar, jagoran musallacin Nuijie, ya kira ga musulmin kasar Sin da na duniya baki daya da su taimaka wajen kawo zaman lafiya da zaman jituwa tare da sauran mutane mabiya addinai daban daban domin tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a doron duniya, haka kuma da yi kira ga girmama rayuwar dan adam tare da jaddada cewa addinin musulunci addini ne na ibada cikin zaman lafiya da zaman jituwa da kaunar juna kamar yadda dokokin musulunci suka tanada.