in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mayakan Boko Haram sun sace matar mataimakin firaministan Kamaru
2014-07-28 09:26:10 cri

A ranar Lahadin nan 27 ga wata, 'yan kungiyar Boko Haram suka yi awon gaba da uwar gidan mataimakin firaministan kasar Kamaru Amadou Ali a wani hari da suka kai a garin Kolofata dake arewacin kasar.

Kamar yadda ministan yada labaran kasar, kuma kakakin gwamnati Issa Tchiroma Bakary ya tabbatar da cewa, an kai harin ne a gidan jami'in gwamnatin dake kusa da kan iyaka da Nigeriya, sakamakon haka, suka yi awon gaba da uwar gidan shi.

Haka kuma an yi awon gaba da wani babban malamin addini a kasar Seini Boukar wanda aka fi sani da Lamido, in ji ministan lokacin da yake tabbatar da wannan lamari ga Xinhua ta wayar tarho.

A kalla mutane 10 ne suka rasa rayukansu a lokacin wannan hari, kamar yadda rundunar sojin kasar suka tabbatar. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China