Kasar Kenya na bullo a yanzu haka da wata dokar da ta shafi kare fasahar gargajiya da duk wasu alamunta na gargajiya na kasar Kenya, in ji wani jami'in gwamnatin kasar. Babban alkalin kasa Githu Muigai ya bayyana a yayin wani taron menama labarai a birnin Nairobi cewa, tuni aka kafa wani kwamitin ministoci da aka baiwa nauyin kafawa da aiwatar wannan doka. A yanzu haka ita wannan dokar, ana rubuta ta, sannan kuma da zaren an amince da ita, to za ta taimaka wajen daidaita kamfanoni masu basira na cikin gida a matsayin tushen wata masana'antar kwarewa ta kasar Kenya, in ji mista Muigai. (Maman Ada)