in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana ci gaba da tattaunawa a game da shirin nukiliya na Iran a Vienna
2014-07-14 10:34:10 cri

Kasar Iran da wasu manyan kasashen duniya sun tattauna a kan shirin nukiliya na Iran, to amma kuma har yanzu akwai banbance-banbancen ra'ayi tsakanin kasar ta Iran da kasashen yammaci.

Ministan harkokin wajen Faransa, Laurent Fabius, ya shaidawa 'yan jarida cewar, za'a ci gaba da tattaunawa, kuma tattaunawar da aka yi a ranar Lahadi ta yi matukar amfani.

To amma tun farko, wasu manyan jami'an diplomasiyya na Amurka da Britaniya sun bayyana cewar, tattaunawar da aka yi a kan rashin daidaiton da aka samu a kan shirin makamashin nukiliya na Iran, a bisa dukkan alamu, ba za a iya samu wata nasara ba a daidai lokacin da aka diba, kila za a cimma yarjejeniya a cikin mako guda mai zuwa. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China