in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta sake bude ofishin jakadancinta a Somalia bayan shekaru 23
2014-07-03 10:36:59 cri

Sabon jakadan kasar Sin, ya gabatar da takardar nadinsa ga ministan harkokin waje na Somalia, Abdirahman Mohammed Beileh a jiya Laraba, wannan shi ne matakin farko na kara bude ofishin jakadancinSin a Somalia, bayan an samu dakon kusan shekaru 23.

Sabon jakadan na Sin a Somalia, Wei Hongtian, ya gabatar da takardar nadi tasa ne a yayin wani buki a ofishin ministan harkokin wajen Somalia.

A jawabinsa, ministan harkokin wajen Somalia, Abdirahman mohammed Beileh, ya yaba da nadin jakadan kasar ta Sin, a inda ya ce, hakan wata alama ce, ta karin matakan tsaro da kuma huldar da kasar ke yi da kasashen duniya. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China