in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya jinjinawa kungiyar AU
2014-06-27 10:03:11 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jinjinawa kungiyar tarayyar Afrika AU a ranar Alhamis game da babban taro karo na 23 da wannan hukuma ta gudana a birnin Malabo, tare da bayyana cewa, kasar Sin na nuna goyon baya sosai ga hadin kan Afrika da tsarin samun makoma mai kyau, da ma dunkulewar wannan yanki.

Abokantaka tsakanin kasar Sin da Afrika na da alfanu da kuma kasancewa tushen samun cigaba ga mutane biliyan 2,3, tare da taimakawa cigaban hadin kai da dangantaka tsakanin kasashen dake samun cigaba, in ji mista Xi.

Duk da sauye-sauyen da ake samu a duniya, kasar Sin za ta cigaba har kullum wajen taimakawa abokin da ba ya da karfi, kuma kasar Sin, abokiyar huldar nahiyar Afrika ce ta gaskiya, in ji mista Xi. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China