in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta Kudu na watsi da duk wani yunkurin tura sojoji a Lesotho
2014-06-20 10:03:55 cri

Gwamnatin Afrika ta Kudu ta kawar da duk wani matakin tura sojoji a kasar Lesotho, dake fama da tashe-tashen hankali dake da nasaba da rikicin siyasa. Ministar harkokin wajen kasar Afrika ta Kudu, madam Maite Nkoana-Mashabane, ta bayyana cewa, duk wani matakin tura sojoji a Lesotho, makwabciyar kasa abu ne da ba ya bisa hanya, duk da cewa, an jibge jami'an tsaro a sassan kasar, da ma kuma kewayen Maseru, babban birnin kasar.

Ba mu da wata yarda kan tura sojoji, amma kuma, muna daga cikin kasashen da suka dauki niyyar tura sojoji a Afrika bisa sa kai, in ji madam Maite Nkoana-Mashabane, ministar harkokin wajen kasar Afrika ta Kudu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China