in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ji karar fashewa kusa da gidan kallon kwallo a jihar Yoben Najeriya
2014-06-18 10:06:40 cri

Wani abu mai kara ya fashe a daf da wani gidan kallon kwallo, yayin da jama'a ke kallon gasar cin kofin duniya a jihar Yobe dake arewa maso gabashin tarayyar Najeriya.

Babban jami'in 'yan sandan yankin Sanusi Rufa'i, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, fashewar ta auku ne a daren ranar Talata yayin da cincirindon jama'a ke tsaka da kallon wasa a birnin Damaturu, fadar mulkin jihar. Ko da yake bai bayyana yawan mutanen da harin ya ritsa da su ba.

Wasu wadanda suka ganewa idanunsu yadda lamarin ya auku, sun ce, sun ji kara mai tsanani, kuma suna zaton harin ya ritsa da mutane da dama. Kana jim kadan da aukuwar hakan, jami'an tsaro sun isa wurin domin gudanar da bincike. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China