in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana za ta karbi bakuncin taro kan harkokin zuba jari
2014-06-12 09:30:55 cri

Wani kamfanin tuntuba game da harkokin zuba jari mai suna "C-NERGY Global Holdings", ya shirya jagorantar babban taron tattaunawa kan hanyoyin da za a bi, wajen bunkasa harkokin hadin gwiwa a fannin zuba jari a kasar Ghana.

Ana dai fatan gudanar wannan taro na karawa juna sani, wanda kamfanin na C-NERGY, da hadin gwiwar ma'aikatar kudi da zuba jarin kasar za su dauki nauyin shiryawa cikin watan Agusta mai zuwa.

Taken taron dai shi ne "shawo kan gibin ababen more rayuwa a Ghana".

Da yake karin haske game da muhimmancin taron, daraktan kamfanin na C-NERGY George Fosu, cewa ya yi, tattaunawar za ta share fagen aiwatar da tsare-tsare masu ma'ana, a fannonin hadin gwiwar zuba jari, karkashin kudurori, da dokoki da tuni aka tsara domin cimma nasarar hakan.

Ita ma a nata bangare, daraktar sashen zuba jari a fannonin da ba na gwamnati ba, ta ma'aikatar kudi da zuba jarin kasar ta Ghana Magdalene Ewurasi Apenteng, cewa ta yi, gwamnatin kasar na fuskantar kalulabe na babban gibi a fannin samar da ababen more rayuwa, don haka akwai bukatar karfafa shigar sassa masu zaman kan su domin cike gibin dake akwai. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China