in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yanke hukunci kan 'yan Habasha fiye da 50 da suka shiga Kenya ba bisa doka ba
2014-06-11 09:40:28 cri

Wasu mutane da ake zargin da shiga kasar Kenya ba bisa doka ba sun bayyana gaban wata kotun Kenya a ranar Talata. An yanke musu zaman gidan yari na shekaru biyu, ko kuma a sake su bayan da suka biya tarar dalar Amurka 114.300. Kuma za'a tusa keyarsu kasarsu idan kusa kammala wa'adin hukuncin nasu. 'Yan kasar waje da dama ne suka amsa kiran jami'an tsaron kasar Kenya a Hadado.

Mutanen sun fito daga birnin Moyale dake kan iyaka da kasashen biyu domin isa birnin Nairobi, a cewar kwamandan 'yan sanda na shiyyar Wajir, mista David Kirui. 'Yan kasar Habasha 32, aka maida kasarsu a makon da ya gabata bayan sun kare zaman yajinsu na watanni shida. 'Yan sandar shiyyar Wajir na fama da matsalar kwararowar bakin haure da dama 'yan asalin kasar Habasha dake shiga wannan kasa ta kan iyakar Wajir. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China