in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi maraba da sabuwar gwamnatin hadin kan Palasdinawa
2014-06-03 20:32:42 cri
Mahukuntan kasar Sin sun yi maraba da sabuwar gwamnatin hadin kan Palasdinawa da aka rantsar ranar Litinin a birnin Ramala da ke gabar yammacin kogin Jordan.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya shaidawa manema labarai cewa, nasarar dinke barakar cikin gida da Paladinawan suka yi, za ta kara karfafa hadin kan al'ummar Palasdinu a kokarin da suke yi na neman kasar Palasdinu tare da samar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin Palasdinu da Isra'ila.

Kasar Sin ta yi imanin cewa, sassantawa cikin lumana, ita ce hanya daya tilo ta tabbatar kasancewar kasashen biyu. Kuma tana fatan Isra'ila da Palasdinu za su warware bambance-bambancen da ke tsakaninsu, kana su koma kan teburin sulhu.

Hong Lei ya yi kira ga kasashen duniya da su goyi bayan wannan yunkuri. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China