in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rantsar da sabuwar majalissar zartaswar Afirka ta Kudu
2014-05-27 09:47:00 cri

A jiya Litinin ne shugaba Jacob Zuma na Afirka ta Kudu, ya rantsar da sabon mataimakinsa Cyril Ramaphosa, yayin bikin kaddamar da sabuwar majalissar zartaswar kasar da aka yi a fadar gwamnati dake birnin Pretoria.

Bayan rantsar da sabon mataimakin shugaban kasar ne kuma, babban mai shari'ar kasar Mogoeng Mogoeng, ya rantsar da ministocin majalissar zartaswar da shugaba Zuma ya nada a ranar Lahadi.

Nadin ministocin 35 dai ya kasance matakin karshe na kafuwar sabuwar gwamnatin kasar, biyowa bayan babban zaben da ya gabata a ranar 7 ga watan nan.

Sabuwar gwamnatin dai ta kunshi sabbin ma'aikatu, da kuma wasu da aka yiwa gyaran fuska, matakin da shugaba Zuman ya ce zai taimaka wajen cimma kudurorin da gwamnatinsa za ta sanya gaba. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China