in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta aika sojoji 80 domin gano 'yan matan Nigeriya da aka sace
2014-05-22 12:09:52 cri

Kasar Amurka ta aika sojoji zuwa kasar Chadi, a kokarin da kasashe suke yi na gano 'yan matan Chibok su fiye da 200 da 'yan Boko Haram suka sace a Nigeriya.

A cikin wasikar da ya aike wa majalisar dokokin Amirka, shugaba Barack Obama ya ce, sojojin Amurkan su kimanin tamanin, za su taimaka wajen tattara bayanai na sirri, da sa-ido, da kuma yin shawagi da jiragen leken asiri a arewacin Najeriya, da kuma yankunan da ke zagayen arewacin Nigeriyar.

Obama ya ce, rundunar dakarun Amurka za ta ci gaba da kasancewa a makwabciyar kasa ta Chadi, har sai an kai wani mataki da ba za a bukaci goyon bayan Chadin ba a wajen warware matsalar sace 'yan matan na Chibok. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China