in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya bukaci Sin da Afrika da su inganta gamayya ta kafofin yada labarai
2014-05-12 10:59:57 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya bukaci kasarsa da Afrika da su zaburar da dangantakar kafofin watsa labarai tsakaninsu.

A yayin da firaministan na kasar Sin ya kai ziyara a ofishin gidan talabijin na kasar Sin CCTV, wanda ke Nairobi, babban birnin kasar Kenya, ya bayyana cewar, kafofin yada labarai na kasar Sin da na Afrika su dinga bayar da rahotanni a kan kasashe masu tasowa ta hanyar amfani da fadar gaskiya, tare da yin adalci wajen bayar da rahotanni, ta yadda za'a dinga baiwa kasashe masu tasowa damar sauraren ra'ayoyin su a duniya.

Li, ya baiwa kafofin yada labarai na kasar Sin, kwarin gwiwa wajen yawaita tsara shirye-shirye masu tsananin inganci domin duniya ta fahimci kasar Sin da Afrika. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China