in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tanzaniya na fatan tura kwararrun harshen Swahili a kasashen yammacin Afrika
2014-05-07 09:27:25 cri

Kasar Tanzaniya ta bayyana fatanta a ranar Talata na tura kwararru a harshen Swahili a cikin kasashen yammacin Afrika, a cikin wani shirin da ya shafi baiwa wannan harshe muhimmin girma a nahiyar.

Da yake jawabi a zauren majalisar dokokin kasar Tanzaniya a Dodoma, hedkwatar kasar, ministar ilimin kasar Tanzaniya, madam Jenista Mhagama ta bayyana cewa, harshen Swahili ya samu babban cigaba a 'yan shekarun baya bayan nan, bisa ga yawan mutanen dake magana da wannan yare, ko kuma suke neman koyonsa.

A shekarar da ta gabata, shugaban kasar Gabon Omar Bongo ya bukaci kasar Tanzaniya da ta tura malaman da za su rika koyar da harshen Swahili a cikin jami'o'in kasarsa, in ji wannan jami'a. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China