in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar kwamitin binciken AU kan Sudan ta Kudu ta isa kasar
2014-04-23 09:50:50 cri

Kwamitin bincike na kungiyar tarayyar Afrika AU kan kasar Sudan ta Kudu na ziyarar aiki ta farko a kasar ta Sudan ta Kudu tun daga ranar 21 ga watan Afrilu har zuwa 1 ga watan Mayu. Wannan rangadi na daga cikin kokarin da kungiyar AU take domin kawo karshen yakin da ya barke a Sudan ta Kudu a cikin tsakiyar watan Disamban shekarar 2013, da kuma tabbatar da samun yanayi mai kyau na wanzar da zaman lafiya mai karko a cikin wannan kasa, in ji wata sanarwa ta AU.

Tawagar za ta gana da shugaban kasar Sudan ta Kudu Slava Kiir Mayardit, da ma wasu sauran manyan jami'an gwamnatin kasar. Haka kuma tawagar ta AU za ta shirya wata ganawa tare da tsohon mataimakin shugaban kasar Riek Machar dake adawa da shugaba Kiir.

Kwamitin na bincike zai gabatar da wani rahoto cikin watanni uku ga kwamitin zaman lafiya da tsaro na kungiyar tarayyar AU. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China