in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An mayar da wadanda hadarin jirgin saman Mozambique ya rutsa da su zuwa Maputo
2014-04-22 14:24:34 cri

An mai da gawawwakin mutane 14, zuwa Maputo, daga cikin gawawwaki 16, 'yan asalin Mozambique, wadanda suka rasa rayukansu, a sakamakon wani hadarin jirgi da aka yi a watan Nawumba da ya gabata a Namibia.

Jirgin saman kasar Mozambique ya yi amanna a bisa cewar, aikin tantance gawawwakin jama'ar da suka rasa rayukansu, wani aiki ne mai wahalar gaske da kuma daukar tsawon lokaci, a inda wani jami'i na jirgin ya kara da cewar, kawo ya zuwa yanzu ana ci gaba da binciken gawawwaki guda biyu, a Namibia domin a tantance su.

A dai ranar 29 ga watan Nawumban da ya wuce ne jirgin saman TM470, wanda an shirya zai je Angola, to amma sai jirgin ya yi hadari a arewa maso gabashin Namibia, a inda a wancan lokacin ya kashe fasinjoji 27, har da wani basine a ciki, da kuma masu aikin kula da jama'a na cikin jirgin har su shida.

Bincike dai ya nuna cewar, matukin jirgin shi ne ya kayar da jirgin yana sane da gangan. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China