Kungiyar tarayyar Afrika AU ta yi kira da a kara rubanya kokari domin warware rikicin Saharawi.
Madam Nkosazana Dlamini-Zuma, shugabar kwamitin kungiyar AU, ta yi maraba da sanarwar ranar 10 ga watan Afrilun shekarar 2014 bisa rahoton babban sakatare na MDD kan rikicin Saharawi, in ji tarayyar AU a ranar Laraba a cikin wata sanarwa.
Wannan rahoto ya kunshe jerin manyan batutuwa, wadanda suke hada da shawarwarin da aka kaddamar ta hanyar tura manzon musammun na sakatare janar na MDD domin tattaunawa tare da bangarori biyun masu gaba da juna, batun ayyakan tawagar MDD kan shirya zaben raba gardama a Saharawi (MINURSO) da kuma ayyukan jin kai da na kare hakkin 'dan adam, in ji wannan sanarwa. (Maman Ada)