in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaron MDD ya bude taron gaggawa kan batun Ukraine
2014-04-14 11:15:43 cri

Wakilan kwamitin tsaron MDD sun fara gudanar da wani taron gaggawa a daren jiya Lahadi, domin tattaunawa kan matsalolin dake addabar gabashin kasar Ukraine, biyowa bayan kwace wata helkwatar 'yan sanda da wasu masu goyon bayan Rasha suka yi a yankin.

Tsakanin watan Fabarairu ya zuwa yanzu dai kwamitin ya kira taruka 10, a yunkurinsa na magance matsalar siyasar dake addabar kasar ta Ukraine. Baya ga yunkurin da babban zaman majalissar ya yi na shiga maganar a ranar 27 ga watan Maris.

Wasu jawabai da aka gabatar yayin zaman na jiya sun nuna cewa, cikin awoyi 24 kadai, akwai a kalla birane 5 da dakaru masu dauke da makamai ke yiwa barazana. Cikin biranen da ke fuskantar irin wannan barazana dai akwai Sloviansk, da Kramatorsk, da kuma birnin Druzhkivka.

Tattaunawar kwamitin tsaron na zuwa a daidai lokacin da mahukuntan Ukraine ke cewa, sun fara daukar matakan yaki da ta'addanci a yankunan gabashin kasar.

A wani ci gaban kuma babban magatakardar MDD Ban Ki-moon, ya bayyana matukar damuwarsa, game da halin da ake ciki na tabarbarewar yanayin tsaro a gabashin kasar ta Ukraine, yana mai kira ga daukacin sassan da abun ya shafa da su kai zuciya nesa, su kuma guji daukar matakan da ka iya rura wutar rikici. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China