in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon zai kai ziyara kasashen Rasha da Ukriane
2014-03-20 10:38:40 cri

Babban sakataren MDD Ban Ki-moon yana kan hanyarsa ta zuwa kasashen Rasha da Ukraine a kokarin da ake na lalubo bakin zaren warware rikicin kasar ta Ukraine cikin ruwan sanyi.

Kakakin Ban Ki-moon ya shaida wa manema labarai cewa, ana sa ran Mr. Ban zai yada zangonsa na farko a Moscow, inda zai gana da shugaba Vladimir Pitun, ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov da sauran manyan jami'an kasar.

A ranar Jumma'a ne ake sa ran Ban ki-moon zai isa Kiev, babban birnin kasar Ukraine inda zai tattauna da mai rikon mukamin shugaban kasar Oleksandr Turchynov, firaministan kasar Arseniy Yatsenyuk da sauran jami'an kasar.

Bugu da kari, Mr. Ban zai gana da mambobin tawagar kare hakkin bil-adama ta MDD da wakilan kungiyoyin fararen hula da ke Kiev. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China