in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magatakardar MDD ya bukaci a kawo karshen banbancin jinsi
2014-03-11 09:36:59 cri

A lokacin bude taron wannan shekarar na kwamitin harkokin mata a MDD, babban magatakardar majalissar Ban Ki-moon a ranar Litinin din nan ya kiran da a kawo karshen banbancin jinsi wanda a cewar shi yana cikin burin da ake son cimmawa a shirin muradun karni da kuma sakamako mai kyau da ake nema bayan shirin a shekara ta 2015.

Mr. Ban da yake jawabi a taro karo na 58 na kwamitin harkokin mata da yanzu haka ake yi a cibiyar majalissar, ya ce, ba za a iya cimma burin martaba juna ba, har sai an samu daidaicin jinsi a ko wane bangare.

Magatakardar majalissar ya yi bayanin cewar, akwai 'yan mata da dama yanzu a makarantun gaba da firamare, amma har yanzu akwai sauran aiki wajen kawo karshen banbancin jinsi a matakai daban daban na bangaren ilimi, yana mai nuni da tazaran dake tsakanin jinsi, musamman a mazaunan karkara da kuma mutane masu fama da nakasa, asalin 'yan kasa da sauran kungiyoyi masu banbanta jinsi.

Za'a kammala wannan taron kwamitin harkokin mata na majalissar a ranar 21 ga watan nan da muke ciki. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China