in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasa Sin ya yi kira ga mahukuntan Malesiya dasu dada kaimi wajen binciko jirgin nan da ya bace
2014-03-08 20:49:28 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya yi kira ga mahukuntan Malesiya dasu dada kaimi, wajen binciko jirgin fasinjan nan da ya bace dauke da mutane 239, ciki hadda 'yan kasar Sin sama da 150.

Mr. Li ya gabatar da wannan kira ne, yayin wata tattaunawa a yau din nan, da takwaransa na kasar ta Malesiyan Najib Razak ta wayar tarho.

A wani ci gaban kuma, hukumar lura da harkokin tekun kasar Sin, ta bayyana cewa, yanzu haka dakarun tsaron gabar tekun kasar sun bazama, zuwa sassan tekun da ake tsammanin jirgin fasinjan nan na kasar Malesiya ya fadi. A shirin su na ceton rayukan mutanen da jirgin ke dauke da su.

Koda yake kawo yanzu ba a tabbatar da inda wannan jirgi ya fadi ba, a hannu guda akwai rade-radin cewa jirgin ya fada wani yankin tekun kasar Vietnam ko Malesiya.

An dai daina jin duriyar wannan jirgi ne, sa'o'i kadan bayan da ya bar filin jirgin Kula Lumfur na kasar Malesiya, a hanyar sa ta zuwa nan birnin Beijing da sanyin safiyar Asabar din nan.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China