in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta damu dangane da rashin tuntubar wani jirgin saman Malesiya
2014-03-08 11:10:28 cri
An kasa tuntubar wani jirgin saman kasar Malesia da ake sa ran zai iso nan Birnin Beijing,kamar yadda hukumar kula da jiragen sama na Sin ta tabbatar.

Jirgin samfurin B777-200 ya taso ne daga Kuala Lampur ne babban birnin kasar Malaysia da misalin karfe 12.41 da safiyar asabar din nan kuma ana sa ran zai sauka Beijing da misalin karfe 6.30 na safiyar yau din a bayanin da kamfanin jiragen saman Malaysia ta bayar.

Hukumar kula da zirga zirgan jiragen saman na Sin ta tabbatar da cewa jirgin mai lambar MH370 yana dauke da Fasinjoji 227 da suka hada da ma'aikatan jirgin 12 da Sinawa 154.

Shi ma Ministan harkokin kasashen wajen Sin Wang Yi a safiyar asabar din nan ya bayyana cewa kasar ta damu matuka game da kasa tuntubar wannan jirgi. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China