in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An hallaka mayakan kungiyar Boko Haram 20 a jihar Bornon Najeriya
2014-03-07 10:35:41 cri

Jami'an tsaro a tarayyar Najeriya, sun ce, dakarun sojin kasar sun harbe mayakan kungiyar nan da aka fi sani da Boko Haram su 20, yayin wani simame da aka kaddamar a sassan jihar Borno.

Wata sanarwa da kakakin ma'aikatar tsaron kasar Chris Olukolade ya fitar jiya a Abuja, babban birnin tarayyar kasar, ta ce, dakarun rundunar sojin sun kuma dakile yunkurin 'ya'yan kungiyar, na kaddamar da wasu hare-hare a unguwannin Ajiri da Mafa, da kuma garin Dikwa da karkarar birnin Maiduguri, helkwatar jihar ta Borno.

Sanarwar ta bayyana cewa, baya ga makamai, da ababen fashewa da aka gano a maboyar 'ya'yan kungiyar, an kuma lalata sansanoninsu dake wurare daban daban, a jihar ta Borno da kuma jihar Adamawa.

Mahukunta a Najeriyar dai sun sha nanata aniyar kakkabe ayyukan kungiya ta Boko Haram daga kasar, musamman ma jahohin arewa maso gabashin kasar, jahohin da suka fi fama da hare-haren magoya bayan kungiyar.

A hannu guda kuma Boko Haram din na dada tsananta kai hare-hare, inda ko da a makon da ya gabata, sai da mayakanta suka hallaka wasu 'yara 'yan makaranta su 29 a jihar Yobe. Kari kan daruruwan fararen hula da suka rasa rayukansu, sakamakon hare-haren kungiyar tun daga shekarar 2009 da ta gabata. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China