in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kimanin mutane 50 ne ake zaton sun rasa rayukansu sakamakon sabon farmaki a Najeriya
2014-02-20 09:39:34 cri

Rahotanni daga jihar Borno dake arewa maso gabashin tarayyar Najeriya, na cewa, kimanin mutane 50 ne ake kyautata tsammanin sun rasu, sakamakon farmakin da 'yan kungiyar Boko Haram suka kaiwa kauyen Bama, na karamar hukumar Bama dake jihar.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa, maharani cike da motoci, sun aukawa kauyen na Bama ne da misalin karfe 4 a asubahin ranar Laraba, suka kuma rika budewa mutane wuta tare da kone gidaje.

Wani wanda ya ganewa idonsa aukuwar lamari ya ce, kimanin gidaje 3000 ne maharani suka lalata.

Da yake tsokaci kan aukuwar wannan lamari, tsohon shugaban kungiyar 'yan kwadago ta Najeriyar Zanna Shettima, wanda 'dan asalin yankin na Bama ne, bayyana harin ya yi da mummunar ta'asa kan al'ummar da ba su ji ba ba su gani ba. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China