Rahotanni daga Sudan ta Kudu na cewa, sojojin Sudan kasar sun tabbatar da cewa, Bantiu, babban birnin jihar Unity mai arzikin mai ya fita daga hannunsu, inda bayanai ke nuna cewa, ana ci gaba da gwabza fada tsakanin sojojin gwamnati da wani rukuni na sojojin da ke biyayya da tsohon mataimakin shugaban kasar Riek Machar.
Ko da yake Mr. Machar ya bayyana a ranar Litinin cewa, a shirya yake ya tattauna da shugaba Salva Kiir Mayardit na kasar Sudan ta Kudu, bisa sharadin cewa, Kiir din ya amince zai saki fursunonin siyasa da ake tsare da su. (Ibrahim)