in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahara sun hallaka mutane 6 a wata kasuwa dake jihar Adamawa
2013-11-23 16:44:24 cri
Rahotanni daga jihar Adamawa dake arewa maso gabshin tarayyar Najeriya, sun tabbatar da rasuwar mutane 6, tare da jikkata wasu da dama, sakamakon wani harin da wasu wadanda ba a san ko su waye ba suka kai Kasuwar Gwari dake kan titin Mubi a ranar Alhamis 21 ga watan nan.

Wasu wadanda suka ganewa idanunsu yadda lamarin ya auku, sun shaida wa majiyar kamfanin dillancin labarun kasar Sin Xinhua cewa, harbe-harben da maharan suka yi ya haddasa yamutsi tare da raunata mutane da yawa.

Rahotannin sun kuma bayyana cewa ba a bude manyan kasuwannin dake birnin Yola ba a jiya Jumma'a, sakamakon binciken da jami'an tsaron suke yi domin tsafke wadanda suka aikata wannan ta'asa.

Kawo yanzu dai, ba a tabbatar da ko kungiyar nan ta Boko Haram ce ta kaddamar da wannan hari ba. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China