in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi maraba da yarjejeniyar da aka cimmawa tsakanin IAEA da Iran
2013-11-12 20:04:43 cri
Kasar Sin a ranar Talatar nan ta yi maraba da yarjejeniyar da aka cimmawa a tsakanin hukumar kula da makamashi ta duniya IAEA da kasar Iran domin masu bincike na hukumar su samu damar duba sansanin makamashin nukiliyar kasar.

A ta bakin kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Sin Qin Gang, kasar a ko da yaushe ta yi imanin cewa, tattaunawa da hadin gwiwa su ne hanyoyin da za a bi a fuskanci wannan matsalar ta makamashin nukiliyar kasar Iran din.

A karkashin yarjejeniyar da aka sanya ma hannu a Tehran, kasar ta Iran za ta amince da jami'an hukumar ta IAEA su ziyarci sansanin sarrafa nukiliya ta Arak da kuma mahakan ma'adinai na Gachin. Abin da a cewar Mr. Qin, wata dama ce mai muhimmanci ta tattaunawa game da batun nukiliyar, don haka Sin na maraba sosai da wannan hadin kai tsakanin bangarorin biyu.

A cewar shi, kasar Sin ta yarda cewa, wannan yarjejeniya za ta taimaka wajen bullo da dabarun warware matsalar nukiliya ta Iran din mai sahihanci kuma yadda ya kamata.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China