in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Najeriya ta amince da karin wa'adin dokar-ta-baci
2013-11-08 10:46:11 cri

A ranar Alhamis 7 ga wata ne, 'yan majalisar dokokin tarayyar Najeriya suka amince da bukatar da shugaban kasar Goodluck Ebele Jonathan ya gabatar musu na kara lokacin dokar-ta-baci a jihohin Borno, Yobe da kuma Adamawa dake arewa maso gabashin kasar da watanni shida, tare da zummar yaki da masu ta da zaune-tsaye.

'Yan majalisar dokokin sun jefa kuri'a ne ba tare da bayyana sunayensu ba, inda baki dayansu suka amince da bukatar da shugaba Jonathan ya gabatar.

A watan Mayu na wannan shekara ne, shugaba Jonathan ya sanar da kafa dokar-ta-baci a jihohin uku, a wani matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na magance hare-haren dake faruwa a yankin, wanda sanadiyyar haka aka tura dubban sojoji zuwa yankin tare da jiragen yaki masu saukar ungulu.

Tuni a ranar Laraba, a cikin wata wasikar da Mr Jonathan ya gabatar, ya ce sojojin Najeriya sun samu nasarori a kan 'yan bindigar yankin, sai dai akwai kalubalen tsaron da yake bukatar a murkushe shi.

Murtala, wakilin sashin Hausa na CRI, daga birnin Ikko, Najeriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China