in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Japan da Rasha za su gudanar da shawarwari a tsakanin ministocin harkokin wajensu da ministocin tsaron kasa a karo na farko
2013-11-02 17:24:47 cri
Ranar 2 ga wata, kasashen Japan da Rasha za su gudanar da shawarwari a tsakanin ministocin harkokin waje da na tsaronsu a karo na farko a birnin Tokyo, hedkwatar kasar Japan. An labarta cewa, wannan shi ne karo na farko da Japan za ta yi irin wadannan shawarwari a tsakaninta da wata kasar da ba su daddale yarjejeniyar zaman lafiya a tsakaninsu ba.

Wasu kafofin yada labarun Japan din sun yi shelar cewa, nufin Japan da Rasha na shirya irin wadannan shawarwari shi ne dakile ci gaban kasar Sin, sai dai nan take Sin da Rasha sun musunta hakan. Madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana cewa, babu wanda zai iya kawo cikas ko lalata bunkasuwar dangantakar abokantaka da hadin gwiwa a tsakanin Sin da Rasha daga dukkan fannoni bisa manyan tsare-tsare. Ta ce, wasu na yunkurin haddasa tunzuri a tsakanin Sin da Rasha, tabbas ne hakarsu ba za ta tarar da ruwa ba.

Har wa yau kuma, Morgulov Igor, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Rasha shi ma ya musunta irin wancan hasashe da wasu kafofin yada labaru na Japan suka yi. Ya kuma jaddada cewa, kasar Sin, abokiyar kasar Rasha ce a fagen hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare. Ya ce, asarsa ta Rasha ba za ta ci dunduniyar kasar Sin a asirce ba.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China