in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in kasar Sin ya gana da shugaban kasar Equatorial Guinea
2013-09-20 17:25:17 cri
Mataimakin babban magatakardan kwamitin ladabtarwa na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, mista Zhao Hongzhu ya kai ziyara a kasar Equatorial Guinea daga ranar 17 zuwa ta 19 ga wata, inda ya gana da shugaban kasar Obiang Nguema Mbasogo.

A lokacin ganawarsu, Mista Zhao ya ce cikin shekaru 43 bayan da kasashen 2 suka kulla huldar diplomasiyya, bangarorin 2 suka samu damar raya huldar dake tsakaninsu sosai, da hadin kai a fannoni daban daban tare da samar da sakamako mai kyau. Kasar Sin ta dora muhimmanci ga kokarin raya huldar dake tsakanin kasashen 2.

A nasa bangaren, shugaba Obiang ya ce, ana gamsuwa da ci gaban huldar dake tsakanin kasashen 2, kana Equatorial Guinea na nuna ma kasar Sin godiya kan tallafin da ta dade tana baiwa kasar Equatorial Guinea.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China