in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An damke mutane 11 da ake zaton 'yan kungiyar Boko Haram a Najeriya
2013-09-16 10:25:47 cri

Jami'in da ke kula da Bataliyan da ke gudanar da ayyuka na musamman a Najeriya, Laftana kanar Beyidi Martins, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua ranar Lahadi cewa, jami'an tsaro na sojoji sun kama wasu mutane 11 a jihar Adamawa da ake zaton 'yan kungiyar Boko Haram ne a wani samame da suka kaiwa 'yan kungiyar.

Laftana kanar Beyidi Martins ya ce, an kama wadanda ake zargin ne a garin Machika ranar Asabar, inda aka garzaya da 6 daga cikin wadanda ake zargin zuwa wani gari da ke kusa da Maiduiguri, biyar daga cikinsu kuma aka kaisu garin Mubi.

Jami'in ya ce, biyu daga cikin 'yan kungiyar ta Boko Haram, sun mutu ranar Lahadi sakamakon raunukan da suka samu, kana daya daga cikinsu yana raye inda ake masa tambayoyi, yayin da guda 3 suka ji rauni sakamakon turjiyar da suka nuna wa sojojin. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China