in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na maraba da daddale yarjejeniya tsakanin Rasha da Amurka kan batun makamai masu guba na Syria
2013-09-15 19:17:50 cri
A ranar Lahadi 15 ga wata, a nan birnin Beijing, ministan harkokin waje na Sin Wang Yi ya gana da takwaransa na Faransa Laurent Fabius, inda suka yi musayar ra'ayi kan batun Syria da sauransu. Wang ya ce, Sin na maraba da daddale yarjejeniya tsakanin Rasha da Amurka kan batun makamai masu guba na Syria, kuma ya amince da shawarar da gwamnatin Syria ta yanke ta shiga tsarin yarjejeniyar hana yin amfani da makamai masu guba.

Wang ya ce, matakin zai sassauta yanayin Syria, tare da samar da makoma mai kyau wajen daidaita batun makamai masu guba na Syria cikin lumana. Sin na fatan za a shigar da batun Syria a karkashin kulawar MDD cikin sauri domin sa kaimi a kai. Kamata ya yi kwamitin sulhu ya taka muhimmiyar rawa kan wannan batu. A sa'i daya, Sin na fatan kungiyar hana yaduwar makamai masu guba za ta gudanar da aikinta cikin adalci kuma bisa goyon bayan kasa da kasa.

Ban da haka, Wang ya jaddada cewa, matakan soja ba za su daidaita matsalar kasar Syria ba, kuma ya kamata a daidaita wannan matsala a siyasance, tare da sa kaimi ga yunkurin lalata makamai masu guba na Syria. Haka zalika mista Wang Yi ya yi kira da a tsagaita bude wuta a tsakanin bangarori masu gaba da juna a Syria, ta yadda za'a samar da yanayi mai kyau wajen soma lalata wadannan makamai da kuma shirya taron duniya na Geneva karo na biyu tun da wuri.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China