Hong Lei ya shaidawa taron manema labarai cewa, yayin da tawagar ke nan kasar Sin, ana saran za ta gana da manyan jami'an ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin inda za su yi musayar ra'ayoyi, yana mai cewa, kasar Sin tana kokarin shiga tsakani da dukkan bangarorin da abin ya shafa game da batun Syria ta hanyar da ta dace.
Mr. Hong ya ce, har kullum kasar Sin tana ganin cewa, hanyar siyasa ita ce mafiya ga batun Syria, kuma kamata ya yi a yi amfani da wannan mataki, musamman a halin da ake ciki yanzu. (Ibrahim Yaya)