in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da taron hukumar siyasa ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta Sin
2013-07-30 21:08:26 cri
An gudanar da taron hukumar siyasa ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta Sin (JKS) a ranar 30 ga wata, inda aka tattauna halin tattalin arziki na kasar a rabin farkon shekarar bana da kuma ayyukan bunkasa tattalin arziki na watanni 6 na karshen shekarar bana. Babban sakataren kwamitin tsakiya na JKS Xi Jinping ne ya shugabanci wannan taro.

A gun taron, an bayyana cewa, yanzu kasar Sin tana cikin muhimmin lokaci na fuskantar kyakkyawar damar samun bunkasuwa, kuma a watanni shida na karshen shekarar bana, kasar Sin za ta kiyaye samun bunkasuwar tattalin arziki yadda ya kamata.

A gun taron, an bukaci hukumomin wurare daban daban na kasar Sin da su ci gaba da aiwatar da manufofin kudi masu yakini da kara nuna goyon baya da matakan bunkasa tattalin arziki, yin kokarin inganta cinikin waje, kyautata manufofi da bada hidima, kara shigar da kayayyaki, yin kokarin tinkarar rikicin ciniki, da kuma sa kaimi ga kamfanoni da su zuba jari a kasashen waje. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China