in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Togo ta hau mukamin shugabancin kwamitin tsaron MDD na karba-karba a watan Mayu
2013-05-02 09:40:27 cri

A ranar llaraba ne kasar Togo ta hau mukamin shugabancin kwamitin tsaron MDD na karba-karba na watan Mayu.

Wakilin din-din-din na kasar Togo a MDD Kodjo Menan shi ne ya karbi ragamar shugabancin kwamitin daga hannun Eugene-Richard Gasana, jakadan kasar Ruwanda a MDD wanda shi ne ya rike matsayin shugaban kwamitin a watan Aprilu.

Wannan shi ne karo na biyu da kasar Togo ta hau matsayin shugabancin kwamitin tun lokaci da aka zabe ta a matsayin mamba wacce ba ta din-din-din ba ga kwamitin na MDD a cikin watan Oktoban 2011.

Ana yin karba-karba na shugabancin kwamitin tsakanin kasashe dake aiki a kwamitin na zaman lafiya da tsaro kowane wata bisa amfani da jerin harrufan Turanci na sunayen kasashen.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China