in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uganda ta dada tsaurara matakan tsaro kan iyakokinta da Jamhuriyar dimokuradiyyar Congo
2013-07-16 10:31:54 cri
Rahotannin baya bayan nan na kasar Uganda na bayyana cewa rundunar sojin kasar ta dauki matakan tsaurara tsaro, a kan iyakokinta da makwabciyarta jamhuriyar dimokuradiyyar Congo, domin magance yiwuwar kwararar mahara daga Congon, biyowa bayan wani dauki ba dadi da dakarun kungiyar 'yan tawayen ADF suka yi da sojojin kasar Congo a Kamango, wani wurin dake kusa da kan iyakar kasashen biyu a ranar Alhamis din da ta gabata, lamarin da ya sanya kimanin mutane 40,000 daga Congon tserewa zuwa Bundibugyo dake kasar Uganda.

Kakakin rundunar sojin kasar ta Uganda Laftana Kanar Paddy Ankunda ne ya tabbatar da daukar wannan mataki, yayin zantawarsa da wakilin kamfanin dillancin labarun kasar Sin Xinhua ta wayar tarho. Rundunar sojin kasar ta Ugandan dai na dari-dari da yiwuwar kwararar mayakan kungiyar ta ADF mai alaka da Al-Qaida, ta hanyar shigarsu ayarin 'yan gudun hijira, daga baya kuma su fara kaddamar da hare-hare a kasar ta Uganda.

A wani ci gaban kuma hukumar MDD mai lura da harkokin 'yan gudun hijira UNHCR ta bayyana cewa, yawan 'yan gudun hijirar dake tururuwa zuwa kasar Uganda daga Congo sun doshi mutum 42,000. A hannu guda ita ma wata kungiyar tallafawa 'yan gudun hijirar mai suna URCS ke nuna halin tsananin bukatar taimako, da 'yan gudun hijirar kasar ta Congo ke ciki a halin yanzu. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China