in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron tattaunawa karo na 4 game da yin gyare-gyare wajen gudanar da ayyukan gwamnatin kasar Sin a birnin Beijing
2013-07-15 16:28:42 cri
A ranar 14 ga wata, an yi taron tattaunawa karo na 4 game da aikin yin gyare-gyare wajen gudanar da ayyukan gwamnatin kasar Sin a birnin Beijing, karkashin taken, gaggauta canja ayyukan gwamnati, don karfafa aikin yin gyare-gyare game da tsarin gudanar da ayyukan gwamnati a kasar. A yayin taron, an dora muhimmanci sosai game da shirin yin gyare-gyare ga tsarin majalisar gudanarwa, da canja ayyukan gwamnati, don nazari da karfafa wannan aiki.

Wakilai da masana mahalartar taron sun ba da shawarwarinsu game da ma'anar yin gyare-gyare game da tsarin gudanar da ayyukan gwamnati, da matakan da za a dauka wajen yin gyare-gyare, da matsalolin da ake fuskanta yanzu, da dai sauransu.

Mataimakin direktan kwamitin kula da tsarin gwamnatin tsakiya na kasar Sin kuma mataimakin shugaban kwamitin nazarin aikin yin gyare-gyare game da tsarin gudanar da ayyukan gwamnati na Sin Wang Feng ya ce, yayin da gwamnatin ke canja ayyukansu, kamata ya yi a canja tunaninsu, sannan kuma, a gudanar da hakikanin matakai bisa tunaninsu, don gudanar da aikin yin gyare-gyare ga tsarin gudanar da ayyukan gwamnatin yadda ya kamata.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China