in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya zama tilas a sa kaimi kan gwamnatin Sham da masu adawa da ita da su yi shawarwarin siyasa cikin hanzari
2013-03-28 20:25:37 cri
An ba da labarin cewa, a yayin taron koli da kungiyar tarayyar kasashen Larabawa wato AL ta shirya a wannan mako a birnin Doha na kasar Qatar, an bai wa masu adawa da gwamnatin kasar Sham wakilcin jama'ar kasar, lamarin da ya jawo suka daga kasar Rasha.

Dangane da wannan, a lokacin da Hong Lei, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin yake amsa tambayoyin manema labaru a nan Beijing a ran 28 ga wata, ya ce, abun gaggawa da za a yi shi ne sa kaimi kan gwamnatin Sham da masu adawa da ita da su yi shawarwarin siyasa da kuma kaddamar da shirin shimfida wani tsarin siyasa na wucin gadi cikin hanzari bisa sanarwar taron ministocin harkokin waje da kungiyar kula da batun Sham ta shirya a birnin Geneva. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China