A hukuncin da shugaban kotun da'ar ma'aikataka Danladi Umar ya yanke a jiya Alhamis, ya ce Walter Onnoghen ya take dokar da'ar ma'aikata, don haka an tube shi daga mukaminsa na Alkalin Alkalan Nijeriya.
Hukuncin na nufin an samu Walter Onnoghen da laifin kin bayyana asalin kadarorin da ya mallaka a lokacin da ya kama aiki.
Kotun da'ar ma'aikatar, ta kuma bada umarnin kwace dukkan kudaden dake cikin asusun da tsohon Alkalin Alkalan ya gaza bayyanawa, inda za a mika su ga gwamnatin tarayyar kasar. (Fa'iza Mustapha)