in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijeriya na da kyakkywan fata game da komawar 'yan matan da ke hannun kungiyar Boko Haram ga iyayensu
2019-04-14 16:17:44 cri
Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ya bayyana kyakkyawan fata game da sakin sauran 'yan matan sakandaren Chibok dake hannun kungiyar Boko Haram.

Cikin wata sanarwa da aka fitar, Muhammadu Buhari, ya sabunta alkawarinsa yayin da ake cika shekaru 5 da sace 'yan matan.

Kimanin 'yan mata 210, na sakandaren garin Chibok na jihar Borno ne aka sace a ranar 14 ga watan Afrilun 2014, inda daga bisani aka saki 107 daga cikinsu, biyo bayan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin gwamnatin da kungiyar.

A wa'adin mulkinsa na farko a shekarar 2015, Shugaban ya yi wa iyayen 'yan matan alkawarin tabbatar da sada su da 'ya'yansu.

Shugaban ya bayyana cewa, wannan alkawarin ne ya sa al'ummar garin Chibok su ka sake zabarsa a zaben da aka yi cikin watan Faburairu.

Ya ce duk da kawo yanzu gwamnatinsa ta yi nasarar karbo 'yan mata 107, ba za ta gajiya ba, har sai ta sada ragowar 'yan matan da iyayensu, yana mai tabbatar da cewa har yanzu gwamnatinsa na aiki kan batun. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China