Xi ya ba da muhimmin umurni kan cikakken zaman taron manyan sakatarorin kwamitin JKS
Daga ranar 19 zuwa ranar 20 ga wata, an yi cikakken zaman taron manyan sakatarorin kwamitin JKS a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. Kafin gudanar taron, babban magatakardan kwamitin tsakiya na JKS, kana shugaban kasar Sin Xi Jinping,ya bada wani umurni, inda ya ce bayan cikakken zaman taron wakilan JKS karo na 18, ya zuwa yanzu, ofisoshin kwamitin tsakiya sun ba da gudummawa matuka wajen raya ayyukan JKS da na kasa baki daya. A don haka, a nan gaba, ya kamata a ci gaba da yin kwaskwarima domin karfafa ayyukan kare ikon kwamitin tsakiya, da kuma aiwatar da ayyukan da kwamitin ya tsara cikin himma da kwazo. (Maryam)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku