in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara sayar da littafi mai taken "Ra'ayoyin Xi Jinping Kan Gudanarwar Harkokin Mulkin Kasa" kashi na biyu a birnin London
2018-04-12 11:03:01 cri
Jiya Laraba 11 ga wata, an yi bikin fara sayar da littafi mai taken "Ra'ayoyin Xi Jinping Kan Gudanarwar Harkokin Mulkin Kasa" kashi na biyu a birnin London na kasar Burtaniya, kuma an wallafa littafin da harsuna daban daban. Dan sarki Andrew, basarake York na kasar Burtaniya wato Andrew Albert Christian Edward da mataimakin shugaban hukumar fadakar da jama'a na kwamitin tsakiyar Jam'iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, kana shugaban ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin Jiang Jianguo sun halarci wannan bikin.

A yayin bikin, dan sarki Andrew ya ce, bikin da aka yi a birnin London ya bada ma'ana kwarai da gaske, domin littafin zai yi bayani ga karin mutane kan kasar Sin, da kuma irin makoma da take nema. Ya kuma nuna fatan cewa, za a sami karin mutane da su kai ziyara a kasar Sin da kansu.

A nasa bangare kuma, Jiang Jianguo ya ce, littafin mai taken "Ra'ayoyin Xi Jinping Kan Gudanarwar Harkokin Mulkin Kasa" ya nuna ci gaban tsarin gurguzu a kasar Sin a yayin da Xi Jinping yake jagorancin kasar. Haka kuma, an yi imanin cewa, ta hanyar karanta wannan littafi, mutanen kasa da kasa za su iya zurfafa fahimtarsu kan Jam'iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, wadda take dukufa wajen tallafawa al'umma, da neman farfadowar kasa da kuma dunkulewar kasa da kasa baki daya.

An fassara littafin zuwa harsuna guda 9, wanda aka fara sayar da su a hukumance bayan bikin da aka yi a birnin London. Kuma wadannan harsuna guda 9 sun hada da bakaken gargajiya na Sinanci, Turanci, Faransanci, Spaniyanci, Jamusanci, Rashanci, Japananci, Larabci da kuma harshen Portugal. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China