in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi zai fara ziyarar aiki a Gabas ta Tsakiya da Afirka kana zai halarci taron BRICS
2018-07-19 14:19:20 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya tashi daga birnin Beijing a yau Alhamis, domin fara ziyarar aiki a hadaddiyar daular Larabawa, kana zai isa kasashen Senegal, da Rwanda, da Afirka ta kudu, inda zai kuma halarci taron koli na 10, na kungiyar BRICS da zai gudana a birnin Johannesburg. Shugaba Xi zai kuma gudanar da ziyarar sada zumunta a kasar Mauritius kafin dawowar sa nan birnin Beijing.

Shugaba Xi dai ya samu gayyata ne daga sarkin masarautar hadaddiyar daular Larabawa Sheikh Khalifa bin Zayed Al Nahyan, da shugaba kasar Senegal Macky Sall, da shugaban Rwanda Paul Kagame, da kuma na Afirka ta kudu Cyril Ramaphosa.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China