in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana ta samu matsayi na 51 a jadawalin hukumar FIFA
2017-11-29 09:52:18 cri

Ghana ta hau matsayi na 51 a bisa alkaluman da hukumar shirya gasar wasannin kwallon kafa ta duniya FIFA ta fitar a ranar Alhamis.

Duk da kasancewa kungiyar wasan Black Stars, ta samu maki 6 inda hakan ya bata damar kara adadin makinta daga jimmalar maki 651 zuwa 657, sai dai ta sauka kasa daga matsayi na 9 a cikin jadawalin jerin sunayen da aka fitar na nahiyar Afrika a cikin wannan wata.

Ghana ta tsallake matsayi guda ne bayan data tashi kunnen doki da Masar a zagayen karshe na gasar share fage na FIFA, wanda aka buga a katafaren filin wasan Cape Coast wanda kasar Sin ta gina.

Senegal ta daga zuwa matsayi na 23, wanda shine matsayi na koli da kasar ta taba kaiwa a wasannin kasa da kasa, tun bayan matsayin farko data taba samu a gasar cin kofin duniya na shekarar 2002.

A halin yanzu kasashen yammacin Afrika sune a bisa matsayin koli a tsakanin kasashen nahiyar ta Afrika, inda suka sha gaban takwarorinsu na Masar da Tunisiya a gasar share fagen cin kofin duniya wanda za'a buga a Rasha a shekarar 2018.

Ghana bata samu damar tsallakewa a gasar ta FIFA ta 2018 ta kasar Rasha ba, sai dai a halin yanzu, ta samu kwarin gwawi na shiga gasar cin kofin kasashen Afrika (AFCON) a shekarar 2019 wanda za'a cigaba da fafatawa a gasar share fagen a watan Maris.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China