in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harin Bangladesh ya rutsa da 'yan kasashen waje da dama
2016-07-03 13:14:48 cri
Harin Bangladesh ya rutsa da 'yan kasar Italiya 9, da 'yan Japan 7, da dan Amurka 1 da 'yan asalin kasar Bangladesh 2, da 'yar kasar Indiya 1 dukkan su na daga cikin mutane 20 da suka rasa rayukan su a sakamakon harin da aka kai a wani wurin cin abinci dake birnin Dhaka, fadar mulkin kasar Bangladesh.

Wani jami'i mai kula da hulda da kafofin watsa labaru na rudunar sojojin kasar Bangladesh ya tabbatar da hakan ga wakilin kamfanin dillancin labaru na Xinhua na kasar Sin a jiya Asabar. Jami'in wanda bai so a ambaci sunansa ba, ya ce cikin wadanda suka mutu akwai maza 10 da mata 10.

'Yan bindiga 7 ne dai suka kai wannan mummunan hari inda suka kashe 'yan sanda 2 a farkon harin, kafin daga bisani su yi awon gaba da wasu 'yan kasashen waje. Sai dai tuni jami'an tsaron kasar Bangladesh suka samu damar kubutar da mutanen 13 da aka yi garkuwa da su a wannan harin.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China