Wakilin majalisar gudanarwar kasar Sin zai kai ziyara kasashen Senegal, Chadi, Malysia, da Indonesiya
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei, ya ce bisa gayyatar da gwamnatocin kasashen Senegal, Chadi, Malaysia gami da ministan shirin tattalin arziki na Indonesiya mista Darmin Nasution suka yi masa, wakilin majalisar gudanarwar kasar Sin mista Yang Jiechi, zai gudanar da ziyarar aiki a kasashen daga ranar 4 zuwa 10 ga watan nan, tare kuma da halartar taro na biyu, na tattauna batutuwan da suka shafi tattalin arziki tsakanin manyan shugabannin Sin da Indonesiya. (Bilkisu)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku