in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin a MDD ya ce, ya kamata ajandar cigaba bayan 2015 ya kunshi habbakar Afrika
2014-07-18 10:58:00 cri

Wakilin din-din-din na kasar Sin, a MDD Liu Jieyi ya shawarci kasashen duniya da su ba da mahimmanci a wajen ci gaban kasashen Afrika yayin da ake zayyana ajandar ci gaban kasashe a bayan shekara ta 2015.

Liu Jieyi wanda ya gabatar da wannan shawarar, a yayin da yake jawabi ga wani babban taron MDD, ya kara da cewar, ba da fiffiko ga ci gaban Afrika, wani babban bangare ne na hadin kai domin zaburar da ci gaban duniya baki daya.

Liu ya kuma yi kira da samar da ingancin muhalli a Afrika, tare da kara karfafa huldar dangantaka na gudanar da ayyuka tare, kana kuma da girmama darajar Afrika da jama'arta. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China