2020-09-17 12:16:15 cri |
A jiya Laraba, shugaban kasar Sin Xi Jinping, wanda ke rangadi a lardin Hunan dake tsakiyar kasar, ya ziyarci wata makarantar firamare dake kauyen Wenming, inda ya yi hira da yara dalibai da suke karatu a makarantar.
Shugaba Xi ya ce, yara manyan gobe ne, wadanda za su tabbatar da makomar al'ummar Sinawa a nan gaba. Don haka ya bukaci daliban da su yi kokarin karatu, ta yadda za su iya samar da gudunmawa ga aikin raya tsarin gurguzu na kasar a nan gaba. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China