![]() |
|
2020-09-17 10:08:59 cri |
Kwamandan runduna ta 66 Ahmed Maslah, ya bayyanawa manema labarai cewa, bayan arangamar sojoji da mayakan na Al-Shabab, sojojin sun kawar da wasu ababen fashewa da 'yan ta'addan suka dasa a hanyar Awdhigle. Maslah ya ce bayan cin lagon mayakan, sojoji sun shiga farautar su lokacin da suke kokarin buya a daji.
Yanzu dai dakarun tsaron gwamnatin Somaliya na kara kaimin daukar matakan soja, a wani yunkuri na ganin bayan mayakan Al-Shabab, dake ta da tarzoma a yankunan kudancin kasar. (Saminu Alhassan)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China